ICPC Za Ta Gurfanar da El-Rufai a Kaduna

ICPC Za Ta Gurfanar da El-Rufai a Kaduna

ICPC Za Ta Gurfanar da El-Rufai a Kaduna

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC na shirin gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa gurfanarwar na daga cikin binciken da hukumar ke yi kan zarge-zargen aikata laifukan cin hanci da rashawa. Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken bayani kan tuhume-tuhumen da ake yi masa ba.

Majiyoyi sun ce za a saurari karar a wata kotu da ke Kaduna, inda ake sa ran El-Rufai zai kare kansa daga zarge-zargen da hukumar ta ICPC ta gabatar.

Wannan mataki na zuwa ne yayin da ICPC ke kara kaimi wajen yaki da cin hanci da rashawa, tare da mayar da hankali kan manyan jami’an gwamnati na yanzu da na baya, domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki a Najeriya.

News Translation in English Language.

ICPC Moves to Arraign El-Rufai Over Alleged Corruption in Kaduna.

The Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission (ICPC) has concluded plans to arraign former Kaduna State Governor, Nasir El-Rufai, before a court in Kaduna over alleged corruption-related offences.

According to reports, the planned arraignment follows ongoing investigations by the anti-graft agency into activities linked to El-Rufai during his time in office. While the exact nature of the charges has not been fully made public, officials say the case forms part of a broader effort to hold public office holders accountable.

Sources familiar with the matter disclosed that the proceedings are expected to commence in Kaduna, where the former governor will be required to enter his plea and respond to the allegations.

The development underscores the ICPC’s renewed push to strengthen its anti-corruption drive, as authorities continue to scrutinize the conduct of both serving and former government officials in Nigeria.

Observers say the case could become a significant test of the country’s commitment to transparency, rule of law, and institutional accountability.

Akwai hasashen rushewar Daular Isra’ila nan da shekarar 2027 - Sheikh Farfesa Mansur Isa Yelwa.

Akwai hasashen rushewar Daular Isra’ila nan da shekarar 2027 - Sheikh Farfesa Mansur Isa Yelwa.

Akwai hasashen rushewar Daular Isra’ila nan da shekarar 2027 - Sheikh Farfesa Mansur Isa Yelwa.

Fitaccen malamin Musulunci a Najeriya, Sheikh Farfesa Mansur Isa Yelwa, ya bayyana cewa akwai hasashen rushewar Daular Isra’ila nan da shekarar 2027.

A cewarsa, tun a shekarar 1998 ne wani shahararren malami, Sheikh Ahmad Yasin, ya yi irin wannan hasashe cewa Daular Isra’ila za ta iya kawo ƙarshe zuwa wannan lokaci.

Farfesa Yelwa ya bayyana hakan ne yayin wata hira da kafar Aljazeera, inda ya ce ya gudanar da bincike mai zurfi kan tarihin Banu Isra’ila. Ya ce a yawancin lokuta, daulolinsu kan ɗauki kimanin shekaru 40 kafin su rushe, sannan daga baya su sake farfaɗowa.

Ya kuma ƙara da cewa bayan fitar da wannan hasashe, an kashe Sheikh Ahmad Yasin bayan wasu shekaru, abin da ya ce ba zai rasa nasaba da irin wannan furuci ba.

Malamin ya bayyana wadannan bayanai ne a cikin wani faifan bidiyo na karatunsa da ke yawo a shafukan sada zumunta.


Amurka ta tura jirage marasa matuƙa Najeriya don yaki da ta’addanci.

Amurka ta tura jirage marasa matuƙa Najeriya don yaki da ta’addanci.

Amurka ta tura jirage marasa matuƙa Najeriya don yaki da ta’addanci.

Amurka ta tura jirage marasa matuƙa (drones) zuwa Najeriya domin tattara bayanan sirri da za su taimaka wajen yaƙi da ta’addanci, tare da tura sojojinta guda 200 don ba da horo ga dakarun Najeriya dake fafatawa da ‘yan ta’adda da suka addabi yankin Arewacin ƙasar.

Wannan na zuwa ne duk da karuwar hare-hare da dawowar Boko Haram musamman a jihar Borno tun bayan isowar sojojin Amurkan.

News Translation in English Language.

US Deploys Drones, Troops to Nigeria to Boost Counterterrorism Efforts.

The United States has deployed unmanned aerial vehicles (drones) to Nigeria to gather intelligence aimed at strengthening the fight against terrorism. In addition, about 200 US troops have been sent to provide training for Nigerian forces engaged in combating insurgents in the northern region of the country.

This development comes amid reports of renewed attacks and a resurgence of Boko Haram activities, particularly in Borno State, despite the recent arrival of US military personnel.
Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ta Yi wa matasa aiki domin ladabtarwa.

Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ta Yi wa matasa aiki domin ladabtarwa.

Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ta Yi wa matasa aiki domin ladabtarwa.

Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, reshen ƙaramar hukumar Sabuwa, ta yi wa wasu matasa masu ɗauke da askin banza aski domin ladabtarwa a yayin bukukuwan Sallah.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, 21 ga Maris, 2026, rundunar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne a wurare daban-daban na garin yayin bikin Sallah da ya gabata.

Shugaban Hisbah na Sabuwa, DC Malam Idris Hayatu, shi ne ya jagoranci wannan aikin.

Sanarwar ta ce: “Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, reshen Sabuwa, ta kaddamar da wani shiri na musamman mai taken Operation Happy Sallah a yau, Asabar, 21 ga Maris, 2026, domin tabbatar da zaman lafiya da tsafta yayin bukukuwan Sallah.”

“An gudanar da aikin ne a sassa daban-daban na garin Sabuwa, inda jami’an suka mayar da hankali wajen hana rashin hankali da dabi’u marasa kyau, da ayyukan kida da ke haddasa hayaniya da taruwar jama’a.”

Shugaban ya kara da cewa hukumar za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda, tare da kare mutuncin jama’a musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.

Haka kuma, ya yi kira ga jama’a musamman matasa su rungumi kyawawan halaye, su guji duk wani hali da ka iya kawo rashin jituwa a cikin al’umma.
Jirgin farko ya sauka a Sabon filin jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa dake Gusau Gabanin Ziyarar Manyan Baƙi.

Jirgin farko ya sauka a Sabon filin jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa dake Gusau Gabanin Ziyarar Manyan Baƙi.

Jirgin farko ya sauka a Sabon filin jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa dake Gusau Gabanin Ziyarar Manyan Baƙi.

Jirgin farko ya sauka a Sabon filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa dake Gusau a wani muhimmin mataki na tarihi, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen karɓar manyan baƙi a jihar Zamfara.

Jirgin, ƙirar Bombardier Challenger 605 da gwamnatin tarayyar Najeriya ke sarrafawa, ya sauka da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi.

A cewar jami’an gwamnati, wannan saukar jirgin gwaji ne da aka gudanar domin tantance shirin filin jirgin kafin zuwan manyan jami’ai da ake sa ran za su ziyarci jihar nan ba da jimawa ba.

Rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da wannan gwaji ne bayan samun amincewa daga ma aikatar kula da zirga-zirgar Jiragen sama ta Najeriya (NCAA), wadda ta bayar da sahalewar domin saukar jirgin.

An kuma gudanar da aikin ne bisa ƙa’idar zirga-zirgar jirage ta gani da ido (Visual Flight Rules – VFR), wato a cikin lokacin rana, daga fitowar rana zuwa faɗuwarta.

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana wannan nasara a matsayin wani babban tarihi, yana mai cewa jihar ta shafe sama da shekaru 30 ba tare da filin jirgin sama mai aiki ba.

Ana sa ran wannan ci gaba zai ƙara jawo hankalin masu zuba jari, da inganta hanyoyin sufuri, tare da buɗe ƙofofin fara zirga-zirgar jiragen kasuwanci a nan gaba.
Jami'ar BUK Ta Kori Dalibai 171 Kan Jabun Takardun Shiga.

Jami'ar BUK Ta Kori Dalibai 171 Kan Jabun Takardun Shiga.

Jami'ar BUK Ta Kori Dalibai 171 Kan Jabun Takardun Shiga.

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta kori dalibai 171 bayan an same su da laifin amfani da jabun takardun shaidar karatu domin samun gurbin karatu a jami’ar.

Rahotanni sun bayyana cewa hukuncin ya biyo bayan wani cikakken bincike da majalisar jami’ar ta gudanar kan sahihancin takardun shiga da daliban suka gabatar lokacin neman gurbin karatu.

A cewar jami’ar, an gano cewa wasu daga cikin daliban sun yi magudi wajen sauya maki a sakamakon jarabawarsu domin su dace da ka’idojin shiga jami’a. Haka kuma, wasu sun yi amfani da takardun wani mutum daban, yayin da wasu bayanansu suka yi sabani da na hukumomin jarrabawa kamar JAMB da WAEC.

Jami’ar ta ce wannan laifi ya saba da dokokinta, wanda ke tanadar da hukuncin kora kai tsaye ga duk wanda aka samu da irin wannan laifi.

A wani bangare kuma, an kori wani dalibi daban saboda cin zarafin masu sanya ido yayin gudanar da jarrabawa.

BUK ta jaddada kudurinta na tabbatar da gaskiya da ingancin ilimi, tana mai gargadin cewa za ta dauki mataki mai tsauri kan duk wanda aka samu da aikata laifin karya dokokin jami’a.

News Translation in English Language.

Bayero University Kano Expels 171 Students Over Falsified Admission Credentials.

Bayero University Kano (BUK) has expelled 171 students after they were found to have used falsified academic credentials to secure admission into the institution.

The decision followed a comprehensive investigation conducted by the university’s Senate, which focused on verifying the authenticity of admission documents submitted by the affected students.

According to the findings, some of the students manipulated their examination scores to meet admission requirements, while others used impersonation by presenting documents belonging to different individuals. In several cases, discrepancies were discovered between the students’ records and official data from examination bodies such as the Joint Admissions and Matriculation Board (JAMB) and the West African Examinations Council (WAEC).

The university stated that such acts constitute a serious violation of its academic regulations, which prescribe expulsion as the appropriate sanction for admission fraud.

In a related development, the institution also expelled another student for assaulting examination invigilators during an exam.

BUK reaffirmed its commitment to maintaining academic integrity and standards, warning that it will continue to enforce strict disciplinary measures against anyone found guilty of violating its rules.
IRGC Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Sansanonin Sojin Isra’ila da na Amurka a Saudiyya.

IRGC Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Sansanonin Sojin Isra’ila da na Amurka a Saudiyya.

IRGC Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Sansanonin Sojin Isra’ila da na Amurka a Saudiyya.

Rundunar kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta sanar da cewa ta kaddamar da sabon zagayen hare-hare kan wasu muhimman wuraren sojin Isra’ila da kuma sansanin sojin Amurka da ke Saudiyya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, IRGC ta ce harin ya kasance kashi na 75 na jerin hare-haren da take kira “Alƙawari na Gaskiya 4”, inda ta yi amfani da makamai masu linzami na zamani domin kai farmaki kan wuraren da take zargin sojojin Isra’ila ke amfani da su.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa an kai hari kan sansanin sojin Amurka na Prince Sultan Air Base da ke ƙasar Saudiyya, wanda ke zama ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin ayyukan sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

IRGC ta ce ta dogara ne da bayanan sirri na leƙen asiri wajen gano wuraren da aka kai wa hare-haren, tare da jaddada cewa tana ci gaba da sa ido kan motsin sojojin Isra’ila da Amurka.

Haka kuma, rundunar ta yi gargaɗin cewa za ta ci gaba da kai hare-hare idan aka ci gaba da abin da ta kira “hare-haren abokan gaba” a yankin.

Sai dai har yanzu babu tabbaci daga wasu kafofin labarai masu zaman kansu dangane da cikakkun bayanai na wannan sabon hari, ciki har da irin barnar da aka yi ko asarar rayuka.

Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin da ke tsakanin Iran, Isra’ila da Amurka ke ci gaba da ƙamari, inda ake fargabar ƙara tsananta rikicin zuwa gaba.

News Translation in English Language.
 
IRGC Launches Fresh Strikes on Israeli Military Sites and US Base in Saudi Arabia.

Iran’s Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC) has announced that it carried out a new wave of attacks targeting key Israeli military sites as well as a United States military base in Saudi Arabia.

In a statement, the IRGC said the operation was the 75th phase of its ongoing campaign, dubbed “True Promise 4,” during which it deployed advanced ballistic missiles against what it described as Israeli military positions.

The statement added that the strikes also targeted the Prince Sultan Air Base in Saudi Arabia, a major hub for US military operations in the Middle East.

According to the IRGC, the attacks were based on intelligence surveillance used to identify Israeli troop locations, stressing that it continues to monitor the movements of both Israeli and US forces.

The force further warned that additional strikes could follow if what it described as “enemy aggression” persists in the region.

However, there has been no independent confirmation from other credible sources regarding the full details of the reported attacks, including the extent of damage or possible casualties.

The development comes amid escalating tensions between Iran, Israel, and the United States, raising concerns about a broader regional conflict.

Muna son dawo da ƙarfin siyasar jihar Kano,” in ji Peter Obi.

Muna son dawo da ƙarfin siyasar jihar Kano,” in ji Peter Obi.

Muna son dawo da ƙarfin siyasar jihar Kano,” in ji Peter Obi.

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, Peter Obi, ya kai ziyara jihar Kano State a ranar Lahadi, inda ya gana da tsohon gwamnan jihar kuma fitaccen ɗan siyasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A yayin ziyarar, Obi ya bayyana cewa manufar ganawar ita ce tattauna hanyoyin dawo da tasirin siyasa da ƙarfin jihar Kano a cikin harkokin ƙasa. Ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin shugabannin siyasa domin ciyar da ƙasa gaba.

Ziyarar ta jawo hankalin jama’a da dama, inda ake ganin na iya zama wata alama ta sabon salon haɗin gwiwa a siyasar Najeriya.
Iran ta ce hare-haren jiragen yaƙin Israi'la da Amurka sun ragu tun bayan harbo jirgin yaƙin Israi'la F-35.

Iran ta ce hare-haren jiragen yaƙin Israi'la da Amurka sun ragu tun bayan harbo jirgin yaƙin Israi'la F-35.

Iran ta ce hare-haren jiragen yaƙin Israi'la da Amurka sun ragu tun bayan harbo jirgin yaƙin Israi'la F-35.

Iran ta bayyana cewa yawan hare-haren jiragen yaƙin Amurka da Isra’ila a tsakiyar ƙasar ya ragu sosai, tun bayan da dakarunta suka harbo wani jirgin yaƙi ƙirar F-35 na Israi'la.

A cewar gidan talabijin na Press TV, wanda ya rawaito daga wani majiyar leƙen asiri da ba a bayyana sunansa ba, tsarin kariyar sararin samaniyar ƙasar ya samu nasarar kai hari kan jiragen abokan gaba, lamarin da ya sa suka rage yawan ayyukan su a sararin samaniyar Iran.

Majiyar ta ƙara da cewa, baya ga wannan hari, dakarun Iran sun kuma lalata kusan jirage marasa matuƙa 200 na Israi'la da Amurka, tare da hana su gudanar da wasu hare-hare a cikin ƙasar.

News Translation in English Language.

Airstrikes by Israel and US Decline After Reported Downing of F-35, Iran Says.

Iran has stated that aerial attacks by Israeli and American warplanes in the central part of the country have significantly decreased following the reported downing of an Israeli F-35 fighter jet by its forces.

According to Press TV, citing an unnamed intelligence source, Iran’s air defense system successfully targeted hostile aircraft, leading to a noticeable reduction in their aerial operations over Iranian territory.

The source further claimed that, in addition to the incident involving the F-35, Iranian forces have destroyed nearly 200 Israeli and US drones, preventing them from carrying out further strikes داخل the country.
Iran Ta Harba Makami Mai Cin Dogon Zango, yayin da IDF Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanarsa ga ƙasashen Turai.

Iran Ta Harba Makami Mai Cin Dogon Zango, yayin da IDF Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanarsa ga ƙasashen Turai.

Iran Ta Harba Makami Mai Cin Dogon Zango, yayin da IDF Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanarsa ga ƙasashen Turai.

Rundunar sojin Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa Iran ta harba wani makami mai linzami mai cin dogon zango a karon farko, wanda ake hasashen zai iya kaiwa nisan kusan kilomita 4,000.

A cewar IDF, wannan ci gaba na nuni da cewa irin wannan makami na iya kai hari zuwa wasu manyan biranen Turai, ciki har da Landan na Birtaniya da Paris na Faransa da kuma Berlin na Jamus.

Rahotanni sun bayyana cewa harba wannan makami na daga cikin matakan da ke kara tsananta rikicin yankin Gabas ta Tsakiya, lamarin da ke haddasa damuwa a tsakanin kasashen duniya kan yiwuwar fadada rikicin zuwa wajen yankin.

Sai dai wasu kasashe, ciki har da Birtaniya, sun jaddada cewa har yanzu babu cikakkiyar hujja da ke tabbatar da cewa akwai barazana kai tsaye ga Turai daga wannan makami.

News Translation in English Language.

IRAN TESTS LONG-RANGE MISSILE, IDF WARNS OF POTENTIAL THREAT TO EUROPE.

The Israeli Defense Forces (IDF) have announced that Iran has, for the first time, launched a long-range ballistic missile believed to have a range of approximately 4,000 kilometers.

According to the IDF, this development suggests that such a missile could potentially reach major European cities, including London in the United Kingdom, Paris in France, and Berlin in Germany.

Reports indicate that the missile launch is part of escalating tensions in the Middle East, raising concerns among the international community about the possible expansion of the conflict beyond the region.

However, some countries, including the United Kingdom, have stated that there is currently no conclusive evidence confirming an immediate or direct threat to Europe from the missile.
Manchester City Ta Lashe Kofin Carabao Na Tara Bayan Doke Arsenal a Wembley.

Manchester City Ta Lashe Kofin Carabao Na Tara Bayan Doke Arsenal a Wembley.

Manchester City Ta Lashe Kofin Carabao Na Tara Bayan Doke Arsenal a Wembley.

Kungiyar Manchester City ta lashe kofin League Cup (Carabao Cup) karo na tara, bayan da ta doke Arsenal da ci 2-0 a wasan karshe da aka buga a filin wasa na Wembley.

Matashin dan wasa Nico O'Reilly ne ya zama tauraron wasan, inda ya zura kwallaye biyu da suka tabbatar da nasarar Manchester City.

Wannan nasara ta kara tabbatar da karfin Manchester City a gasar, yayin da suke ci gaba da kafa tarihi a fagen kwallon kafa na Ingila.

News Translation in English Language.

Manchester City Win Ninth Carabao Cup After Defeating Arsenal at Wembley.

Manchester City secured their ninth League Cup (Carabao Cup) title after a 2–0 victory over Arsenal in the final held at Wembley Stadium.

Young talent Nico O'Reilly emerged as the standout performer of the match, scoring both goals that sealed the triumph for Manchester City.

The victory further underlines Manchester City's dominance in the competition, as they continue to cement their legacy in English football.
Hari Kan Asibiti a Sudan Ya Kashe Mutane 64, Ciki Har da Yara 13

Hari Kan Asibiti a Sudan Ya Kashe Mutane 64, Ciki Har da Yara 13

Hari Kan Asibiti a Sudan Ya Kashe Mutane 64, Ciki Har da Yara 13

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa wani mummunan hari da aka kai kan wani asibiti a ƙasar Sudan ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 64, ciki har da yara 13.

A cewar rahotanni, harin ya kuma jikkata mutane da dama, yayin da ake ci gaba da fama da rikici mai tsanani a ƙasar, wanda ke haddasa babbar asarar rayuka da dukiyoyi ga fararen hula.

Hukumar ta WHO ta nuna matuƙar damuwa kan yadda ake kai hare-hare kan cibiyoyin kiwon lafiya, tana mai jaddada cewa irin waɗannan ayyuka na barazana ga rayuwar marasa lafiya da ma’aikatan lafiya, tare da ƙara ta’azzara matsalar jin kai a Sudan.

Rikicin da ke ci gaba da gudana a Sudan ya janyo lalacewar muhimman ababen more rayuwa, musamman a bangaren lafiya, lamarin da ke sa samun kulawa ga marasa lafiya ya ƙara zama ƙalubale.

Hukumar ta WHO ta yi kira ga dukkan ɓangarorin da ke rikicin da su mutunta dokokin ƙasa da ƙasa, musamman waɗanda ke kare fararen hula da cibiyoyin lafiya.
Iran ta kai Hari kusa da cibiyar Nukiliyar Israi'la inda mutum 6 Suka muta tare da jikkata mutum 100.

Iran ta kai Hari kusa da cibiyar Nukiliyar Israi'la inda mutum 6 Suka muta tare da jikkata mutum 100.

Iran ta kai Hari kusa da cibiyar Nukiliyar Israi'la inda mutum 6 Suka muta tare da jikkata mutum 100.

Iran ta Kai munanan harin Makami Mai Linzami a kusa da cibiyar Nukiliyar Israi'la inda Mutane 6 Suka mutu, yayin da sama da mutane 100 Suka Jikkata a Arad, dake Kudancin Isra’ila.

Kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya ruwaito cewa an kwashe mutane 64 da suka jikkata daga wurin da harin ya afku, ciki har da mutum 7 da ke cikin mawuyacin hali, yayin da wasu 15 ke cikin matsakaicin hali.

Haka kuma, majalisar ministocin Isra’ila na gudanar da wani taron gaggawa ta wayar tarho domin tattauna halin da ake ciki bayan hare-haren da aka kai a Dimona da kuma Arad.

A wani ɓangare, rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewa wani makami mai linzami na Iran mai nauyin kilogram 450 ya faɗi a cikin birnin Arad, inda ta amince cewa ba ta samu nasarar kakkabe shi ba kafin ya faɗo.

News Translation in English Language.

Iranian Missile Strike Kills 6, Injures Over 100 Near Israel’s Nuclear Facility.

At least six people have been confirmed dead and more than 100 others injured following a major Iranian missile strike near Israel’s nuclear facility in Arad, southern Israel.

According to reports by Anadolu Agency, 64 injured victims were evacuated from the scene, including seven in critical condition and 15 in moderate condition.

In response to the attack, Israel’s cabinet held an emergency phone meeting to assess the situation, particularly following strikes reported in Dimona and Arad.

Meanwhile, the Israeli military confirmed that a 450-kilogram Iranian missile struck the city of Arad, acknowledging that it failed to intercept the projectile before impact.

The incident comes amid escalating tensions between Iran and Israel, raising further concerns across the international community.