Iran Ta sanar da Dakatar da Hare-haren makamai masu linzami kan Israi'la.
Iran Ta sanar da Dakatar da Hare-haren makamai masu linzami kan Israi'la.

Ƙasar Iran ta sanar da dakatar da hare-haren soji da take kai wa Isra’ila, tana mai cewa dakarunta sun gudanar da martani mai ƙarfi game da Hare-haren da Israi'la ke kai Lebanon, tare da gargadin cewa duk wani sabon rikici zai iya haifar da sake ɗaukar matakan soji.

A wata sanarwa da rundunar tsaron Iran ta fitar a yau Litinin, ta ce an dakatar da ayyukan sojin ne bayan wasu hare-haren makamai masu linzami da aka kai kan wasu wuraren sojin Isra’ila.

Mahukuntan Iran sun bayyana cewa an kai hare-haren ne a matsayin martani ga ayyukan sojin Isra’ila a kudancin Lebanon da kuma yankunan kudancin Beirut. 
Sun kuma ce an kai hare-haren kan wasu sansanonin jiragen saman sojin Isra’ila da Tehran ke zargin suna da hannu a hare-haren da ake kai wa Lebanon.

Sanarwar ta ce dakatar da ayyukan sojin ba yana nufin Iran ta rage shirin kare kanta, tana mai jaddada cewa dakarunta suna cikin cikakken shiri idan rikici ya sake barkewa.

Mai magana da yawun hedikwatar rundunar, Birgediya Janar Ebrahim Zolfaghari, ya ce dakarun Iran sun nuna cikakken ƙarfin kai hari da kuma kare kai a lokacin farmakin. Ya yi gargadin cewa duk wani sabon hari kan Iran ko ƙawayenta a yankin zai fuskanci martani mafi tsauri.

Iran ta kuma zargi Amurka da goyon bayan Isra’ila a rikicin yankin, tana mai cewa Amurka na da alhakin ƙaruwar tashin hankalin da ake gani a halin yanzu.

Iran ta sake jaddada matsayinta cewa zaman lafiya a yankin zai samu ne idan aka dakatar da ayyukan soji a Lebanon tare da mutunta yarjejeniyoyin tsagaita bude wuta da ake da su.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar tashin hankali a Gabas ta Tsakiya, inda hare-haren da ake musayarwa tsakanin bangarori daban-daban suka kara haifar da fargabar yiwuwar rikicin ya bazu zuwa wasu sassan yankin.

Duk da cewa Iran ta ce ta dakatar da hare-haren da take kaiwa a yanzu, jami’anta sun bayyana cewa za su ci gaba da sanya ido kan halin da ake ciki, kuma duk wani mataki na gaba zai dogara ne da yadda al’amura za su gudana.

Sabbin abubuwan da suka faru sun kara nuna ci gaba da takun-saka tsakanin Iran da Isra’ila, yayin da kowanne bangare ke zargin ɗayan da haddasa rashin zaman lafiya da matsalolin tsaro a yankin.
Unsafe Food Causes 53,000 Deaths Annually in Nigeria – FG
Unsafe Food Causes 53,000 Deaths Annually in Nigeria – FG
The Federal Government has raised concerns over the growing threat of foodborne diseases, revealing that unsafe food causes more than 53,000 deaths and nearly 50 million illnesses in Nigeria every year.

Speaking at a ministerial briefing in Abuja to mark the 2026 World Food Safety Day, Nigeria’s Minister of State for Health and Social Welfare, Iziaq Salako, described food safety as a major public health and national development issue.

According to the minister, foodborne diseases result in an estimated 4.26 million years of healthy life lost annually due to illness, disability, and premature death.

“Nigeria records nearly 50 million foodborne illnesses every year, while unsafe food is responsible for more than 53,000 deaths annually,” Salako said.

He noted that children under the age of five bear the greatest burden, accounting for more than 80 percent of foodborne disease cases in the country. He warned that the impact extends beyond illness and death, affecting children's physical, cognitive, and developmental potential.

Salako cited diarrhoeal diseases as the leading foodborne health challenge in Nigeria, with over 40 million cases linked to pathogens such as Salmonella, E. coli, Campylobacter, Shigella, and rotavirus.

He also expressed concern over rising exposure to chemical contaminants, particularly lead contamination in grains, spices, and water sources, which contributes to significant health losses.

The minister referenced recent estimates by the World Health Organization, which indicate that unsafe food causes about 866 million illnesses and 1.5 million deaths globally each year, with Africa carrying the highest per-capita burden.

Despite the challenges, Salako said Nigeria has made progress in strengthening its food safety systems. He highlighted improvements recorded during the country’s 2023 Joint External Evaluation and noted that Nigeria’s 2025 State Party Annual Report score exceeded WHO targets for low- and middle-income countries.

He called for stronger surveillance of chemical contaminants, improved food safety practices in traditional markets, better sanitation infrastructure, and stricter compliance with national food standards.

The minister also linked food safety to the growing prevalence of non-communicable diseases such as hypertension, diabetes, obesity, and stroke. He disclosed that Nigeria has developed sodium reduction guidelines and is implementing industrial trans-fat elimination regulations while reviewing measures to strengthen taxes on sugar-sweetened beverages and improve food labeling systems.

Also speaking at the event, Director-General of the National Agency for Food and Drug Administration and Control, Mojisola Adeyeye, said food safety remains critical to public health and national development.

Represented by Eva Edwards, Director of Food Safety and Applied Nutrition, Adeyeye stressed that reducing foodborne diseases requires science-based regulation, effective surveillance, and stronger collaboration among government agencies, industry stakeholders, researchers, and consumers.

Meanwhile, the advocacy group Corporate Accountability and Public Participation Africa urged the government to adopt tougher regulations on unhealthy foods and beverages. The organization warned that excessive consumption of sugar, salt, unhealthy fats, and ultra-processed foods is contributing to rising rates of hypertension, diabetes, obesity, kidney disease, and certain cancers.

CAPPA welcomed efforts to strengthen Nigeria’s Sugar-Sweetened Beverage Tax and called for the introduction of front-of-pack warning labels, sodium reduction targets, and tighter restrictions on marketing unhealthy foods to children.

World Food Safety Day is observed annually to promote awareness and action aimed at preventing, detecting, and managing food-related risks. The 2026 edition was celebrated under the theme, “From Burden to Solutions – Safe Food Everywhere.”
Abbas Pushes for Data Reform, Says Reliable Statistics Key to Nigeria’s $1 Trillion Economy Goal
Abbas Pushes for Data Reform, Says Reliable Statistics Key to Nigeria’s $1 Trillion Economy Goal

The Speaker of the House of Representatives, Tajudeen Abbas, has stressed that Nigeria cannot achieve its ambition of becoming a $1 trillion economy without a modern and dependable statistical system.

Speaking at a public hearing on the proposed Statistics Bill 2025 in Abuja, Abbas said accurate and timely data must form the foundation of government policies, budget decisions, and development planning.

Represented by House Leader Julius Ihonvbere, the Speaker described the current Statistics Act of 2007 as outdated and no longer suited to the realities of a rapidly evolving digital world.

According to him, the proposed legislation seeks to replace the existing law with a stronger framework that will enhance the capacity of the National Bureau of Statistics, improve data governance, ensure sustainable funding, and support the use of emerging technologies in statistical operations.

“To plan without accurate data is to build a house on quicksand,” Abbas said, noting that credible statistics are essential for economic growth, infrastructure development, poverty reduction, and effective governance.

The bill aims to modernise Nigeria’s National Statistical System by strengthening coordination among government agencies, promoting digital data collection and dissemination, improving quality assurance mechanisms, and reducing duplication in data gathering efforts.

Abbas said the reforms would help build confidence in official statistics among investors and development partners both within and outside Nigeria.

He also called on stakeholders from government institutions, academia, civil society organisations, and the private sector to contribute to the legislative process to ensure the final law addresses current and future challenges in data management.

Supporting the bill, Adeyemi Adeniran, Statistician-General of the Federation and Chief Executive Officer of the National Bureau of Statistics, said Nigeria’s statistical system must adapt to technological changes and the growing importance of data-driven decision-making.

Adeniran explained that the proposed law would strengthen institutional coordination, encourage innovation in data production, and improve the availability of reliable statistics for policymaking and national development.

He added that the bill contains 42 clauses covering statistical governance, data management, funding, accountability, confidentiality, and stakeholder collaboration.

If passed, the Statistics Bill 2025 is expected to become the most significant reform of Nigeria’s official statistical system in nearly two decades, providing a stronger foundation for evidence-based governance and economic planning.
Somali World Cup Referee Denied Entry into United States
Somali World Cup Referee Denied Entry into United States

Award-winning Somali referee Omar Artan, who was set to become the first official from Somalia to officiate at a FIFA World Cup, has reportedly been denied entry into the United States ahead of the 2026 tournament.

According to Somali sports officials, Artan was stopped at Miami International Airport despite holding a valid U.S. visa. The reason for the decision was not immediately disclosed, although Somalia is among countries affected by recent U.S. travel restrictions.

A senior adviser to Somalia's Ministry of Youth and Sports, Ciise Aden Abshir, described Artan as one of Africa's most respected referees and said the decision was a setback for both the official and the sport.

Artan has since returned to Istanbul, where he had been residing. Officials argued that preventing him from participating in the tournament undermines football's principles of fairness, merit, and equal opportunity.

The referee was among the 52 match officials selected by FIFA for the 2026 World Cup, which is being hosted jointly by Canada, Mexico, and the United States.

Since becoming a FIFA referee in 2018, Artan has officiated in Somalia's top football league and worked at major continental competitions, including the Africa Cup of Nations. In 2025, he was named Africa's Men's Referee of the Year by the Confederation of African Football.

Earlier this year, Somali President Hassan Sheikh Mohamud praised Artan's achievement, describing him as an inspiration to young Somalis after becoming the country's first referee selected for a FIFA World Cup.
Shugabannin Musulmi a jihar Oyo Sun Gudanar da Addu’o’i Don Kawo Karshen Garkuwa da Mutane da Ta’addanci
Shugabannin Musulmi a jihar Oyo Sun Gudanar da Addu’o’i Don Kawo Karshen Garkuwa da Mutane da Ta’addanci

Shugabannin Musulmi da mabiya addinin Musulunci daga sassa daban-daban na Jihar Oyo sun taru a filin addu’a na Yidi da ke Agodi, Ibadan, domin neman taimakon Allah game da karuwar matsalolin tsaro da suka hada da garkuwa da mutane da fashi da makami da sauran ayyukan ta’addanci a jihar.

Taron addu’ar, wanda aka gudanar da amincewar Babban Limamin Ibadan, Abdulganiy Agbotomokekere, ya samu halartar malamai da shugabannin al’umma da daruruwan mabiya daga kananan hukumomi 11 na yankin Ibadan.

Masu jawabi a wajen taron sun jaddada cewa hadin kai tsakanin ‘yan Najeriya, tare da yawaita addu’o’i, na daga cikin manyan hanyoyin da za su taimaka wajen shawo kan matsalolin rashin tsaro da ke addabar kasar.

Malam Muyideen Onihantu, wanda ya gabatar da lakca a taron, ya ce manufar addu’ar ita ce neman taimakon Allah domin kawo karshen rashin tsaro da ya hana jama’a zaman lafiya.

Ya bayyana cewa taron ba na kabilar Yarbawa kadai ba ne, domin mambobin al’ummomin Hausawa da Nufawa da Tapa ma sun halarta, abin da ya nuna muhimmancin hadin kai wajen magance matsalolin tsaro.

Shi ma Babban Limamin Sabo, Ibrahim Abdullahi, ya bukaci gwamnati ta kara kaimi wajen kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su tare da inganta matakan tsaro domin dakile irin wadannan hare-hare.

A nasa bangaren, Sakatare Janar na Kungiyar Musulmin Jihar Oyo, Abidemi Siyanbade, ya nuna damuwa kan yadda ‘yan bindiga ke kara kutsawa yankunan jihar, yana mai gargadin cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, matsalar na iya bazuwa zuwa sauran yankunan Kudu maso Yamma.

Ya kuma yi watsi da ikirarin cewa masu aikata wadannan laifuka suna da alaka da addinin Musulunci, yana mai cewa su masu laifi ne kawai da ke haddasa rashin zaman lafiya a kasa.

Siyanbade ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika bai wa jami’an tsaro bayanan sirri kan duk wani abu da suka gani na zargi a yankunansu, yana mai cewa tabbatar da tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.

Shugaban dalibai Muslim na Najeriya, Mustafa Olumide, ya ce dalibai na daga cikin wadanda matsalar rashin tsaro ta fi shafa. Ya gargadi cewa idan ba a dakatar da garkuwa da mutane ba, iyaye da dama za su fara cire ‘ya’yansu daga makarantu saboda fargabar tsaro.

A karshe, shugabannin Musulmin sun yi addu’ar samun nasarar kubutar da duk wadanda ke hannun masu garkuwa da mutane tare da dawowar zaman lafiya da tsaro a Jihar Oyo da Najeriya baki daya.
Isra'ila Ta Kai Harin Ramuwar Gayya Kan Iran Bayan Harin Makamai Masu Linzami da Iran ta Kai cikin Israi'la.
Isra'ila Ta Kai Harin Ramuwar Gayya Kan Iran Bayan Harin Makamai Masu Linzami da Iran ta Kai cikin Israi'la.

Isra'ila ta kaddamar da hare-haren sama kan wasu wuraren soji a yammaci da tsakiyar Iran bayan Iran ta harba jerin makamai masu linzami zuwa arewacin Isra'ila, lamarin da ya kara tsananta rikicin da ke tsakanin kasashen biyu tun bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a watan Afrilu.

Sojojin Isra'ila sun bayyana cewa jiragen yakinsu sun kai hare-hare kan wuraren soji da suka danganta da hukumomin tsaron Iran. Rahotanni sun ce an ji karar fashe-fashe a Tehran da Isfahan da Tabriz da kuma yankunan da ke kusa da Karaj. 
Sai dai hukumomin Iran sun ce ba a kai hari kan unguwannin birnin Tehran ba, kuma babu rahoton asarar rayuka nan take.

Rikicin ya kara kamari ne bayan rundunar Kare juyin juya halin Musulunci ta Iran, IRGC ta harba makamai masu linzami zuwa arewacin Isra'ila, inda ta bayyana harin a matsayin farkon jerin hare-haren da za su ci gaba har na tsawon mako guda. 
Israi'la ta Yi Ikirarin cewwa tsarin kariyar sararin samaniyarta ya yi nasarar kakkabo mafi yawan makaman, sannan daga baya aka ba mazauna yankunan da abin ya shafa damar fita daga mafaka.

Tashin hankalin ya biyo bayan hare-haren da Isra'ila ta kai kan wuraren da take zargin na Hezbollah ne a kudancin Beirut a ranar Lahadi. 
Iran ta gargadi cewa duk wani sabon hari da za a kai kan Lebanon ko muradunta zai fuskanci martani mai tsauri.

A halin da ake ciki, Shugaban Amurka Donald Trump ya bukaci bangarorin su nuna hakuri tare da kauce wa kara rura wutar rikici. Rahotanni sun ce ya tattauna da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, inda ya bukace shi da kada ya mayar da martani domin kada hakan ya kawo cikas ga kokarin diflomasiyya da ake yi.

Sabon tashin hankalin ya kuma yi tasiri ga harkokin tsaro da tattalin arziki a yankin. 
Iran ta dakatar da dukkan jiragen da ke shigowa Filin Jirgin Sama na Imam Khomeini da ke Tehran, yayin da farashin danyen mai ya tashi sakamakon fargabar katse hanyoyin samar da makamashi daga Gabas ta Tsakiya.

Kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da dama sun yi kira ga bangarorin da su rage zafin rikicin tare da komawa teburin tattaunawa, suna gargadin cewa ci gaba da hare-haren juna na iya jefa yankin cikin wani babban rikici mai fadin gaske.
Rukunin farko na Alhazan Jihar Kwara Su 560, sun Dawo Gida Bayan Kammala aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya.
Rukunin farko na Alhazan Jihar Kwara Su 560, sun Dawo Gida Bayan Kammala aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya.

Rukunin farko na Alhazan Jihar Kwara Su 560 sun dawo lafiya zuwa Ilorin bayan kammala aikin Hajjin shekarar 2026 a ƙasar Saudiyya.

Alhazan sun sauka a Filin Jirgin Sama na Babatunde Idiagbon da ke Ilorin a yau Lahadi da misalin ƙarfe 12:23 na rana, ta hanyar jirgin Max Air, tare da jami’ai uku daga Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON).

Hukumar Kula da Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta tabbatar da isowarsu a cikin wata sanarwa da sakatariyar yada labarai, Jumoke Jimoh ta fitar.

Bayan saukarsu, wasu daga cikin alhazan sun bayyana godiyarsu ga Allah bisa nasarar kammala aikin Hajji cikin aminci da kwanciyar hankali.

Shugaban alhazai, Uthman Iyanda-Muhammad, ya bayyana cewa wannan shekarar ta kasance ta musamman, inda ya yaba wa gwamnatin jihar Kwara bisa inganta jin daɗin alhazai, musamman samar da abincin gida.

Sauran alhazai sun kuma yaba da yadda aka tsara tafiyar Hajjin, ciki har da masauki da abinci da kuma sufuri cikin tsari mai kyau.

Wata alhajiya, Rasheedat Saka, ta nuna godiya ga gwamnati bisa tabbatar da cewa aikin Hajji ya gudana ba tare da manyan matsaloli ba.

Iyalai da abokai da sauran jama’a sun tarbi alhazan a filin jirgin sama cikin farin ciki da murna yayin dawowarsu lafiya.

Hukumar ta kuma bayyana cewa ana sa ran isowar rukuni na biyu a ranar Talata, tare da tabbatar da cewa an kammala duk shirye-shiryen tarbarsu.
Iran ta harba makamai masu linzami zuwa cikin Isra’ila.
Iran ta harba makamai masu linzami zuwa cikin Isra’ila.

Rundunar Sojin Iran ta sanar da kai harin makamai masu linzami a wasu yankunan Isra’ila, kamar yadda kafar labarai ta Press TV ta ruwaito.

An bayyana harin a matsayin martani ga ci gaba da hare-haren da Isra’ila ke kaiwa a Lebanon, wanda Iran ke zargin cewa sun karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta, tare da kai farmaki a yankunan fararen hula a kudancin Beirut da kudancin Lebanon.

Rahotanni daga kafafen labarai na Isra’ila sun ce an ji karar kararrawar gargadi a wurare da dama a arewa da tsakiyar ƙasar, ciki har da Haifa da Nazareth da Safed da Tiberias da tuddan Golan. 
Hukumomin Isra’ila sun kuma ce an sanya tsarin kariya na iska cikin shirin gaggawa tare da rufe makarantu saboda dalilai na tsaro.

Jagororin sojin Iran sun yi gargadi cewa idan hare-haren Isra’ila a Lebanon suka ci gaba, za a iya fuskantar ƙarin hare-hare masu tsanani. 
Sun kuma zargi Isra’ila da ƙara tsananta rikici a Lebanon, ciki har da amfani da makamai da aka haramta a duniya, kodayake ba a tabbatar da wannan ikirari daga wata tushe mai zaman kanta ba.

Rahoton ya kuma ce Iran ta taba gargadi cewa za ta mayar da martani idan aka faɗaɗa hare-hare zuwa kudancin Beirut, tare da jaddada cewa ci gaba da rikicin zai haifar da mummunan sakamako.
Gwamnatin jihar Kano Za Ta Fara Gwajin Lafiya Ga Ma’aurata 3,000 Kafin Shirin Auren Gata.
Gwamnatin jihar Kano Za Ta Fara Gwajin Lafiya Ga Ma’aurata 3,000 Kafin Shirin Auren Gata.

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kammala shirye-shiryen gudanar da gwajin lafiya ga ma’aurata 3,000 da suka yi rajista domin shiga shirin auren gata da gwamnatin jihar ke shiryawa.

Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Sheikh Mujahedeen Aminudeen, ya bayyana cewa za a fara gudanar da gwajin ne daga ranar Litinin, 8 ga Yuni, 2026, a kananan hukumomi 24 na jihar.

A cewarsa, ma’auratan sun hada da mata 1,500 da maza 1,500, kuma za a yi musu gwaje-gwaje domin tantance lafiyarsu kafin a daura musu aure.

Ya ce an shirya gudanar da gwajin ne tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano da Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano.

Gwaje-gwajen da za a yi sun hada da na cutar HIV/AIDS da hepatitis B  da tantance jinsin halitta (genotype) da amfani da miyagun kwayoyi da ciwon sanyi (gonorrhoea) da sauran cututtukan da ake dauka ta hanyar jima’i.

Aminudeen ya ce an umurci duk wadanda suka yi rajista da su je ofisoshin Hisbah da ke kananan hukumominsu domin gudanar da gwajin, yana mai gargadin cewa duk wanda bai halarta ba za a cire sunansa daga cikin wadanda za su amfana da shirin.

Ya kara da cewa wadanda suka samu sakamakon gwaji mai gamsarwa ne kawai za su cancanci shiga cikin shirin auren.

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta sake dawo da shirin auren gata domin taimaka wa marasa karfi wajen yin aure da kuma rage wasu matsalolin zamantakewa da suka hada da karuwanci da sauran dabi’u marasa kyau a tsakanin matasa.
Dan Takarar Gwamnan NDC a jihar Kano, Aminu Gwarzo Ya bayyana Alhininsa game da Rasuwar Tsohon Mai Watsa Labarai Adamu Getso.
Dan Takarar Gwamnan NDC a jihar Kano, Aminu Gwarzo Ya bayyana Alhininsa game da Rasuwar Tsohon Mai Watsa Labarai Adamu Getso.

Dan takarar gwamnan jihar Kano na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC), Aminu Gwarzo, ya bayyana alhininsa kan rasuwar fitaccen dan jarida kuma tsohon shugaban kafafen yada labarai na gwamnati, Alhaji Adamu Getso.

Rahotanni sun ce Getso ya rasu ne a ranar Asabar a garinsa na Getso da ke karamar hukumar Gwarzo a jihar Kano.

Marigayin ya taba zama Manajan Darakta na gidan Talabijin din Abubakar Rimi (ARTV), sannan ya kuma rike mukamin Manajan Darakta na Radiyon jihar Kano a wa’adin mulki na biyu na tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

A cikin sakon ta’aziyya da kakakinsa Ibrahim Shuaibu ya fitar a ranar Lahadi, Gwarzo ya bayyana marigayin a matsayin gogaggen dan jarida kuma kwararren mai yada labarai wanda gudunmawar da ya bayar wajen bunkasa harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a a Kano za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa.

Ya ce Adamu Getso ya sadaukar da wani babban bangare na rayuwarsa wajen yi wa al’umma hidima ta hanyar aikin yada labarai, inda ya bar kyakkyawan tarihi na kwarewa da rikon amana da jajircewa wajen bautar jama’a.

Gwarzo ya ce rasuwar tasa babban rashi ne ba ga iyalansa kadai ba, har ma ga daukacin al’ummar Kano da kuma bangaren yada labarai baki daya.

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya sanya shi cikin Aljannatul Firdaus, sannan Ya bai wa iyalansa da masoyansa hakurin jure wannan babban rashi.
Zulum ya yabawa sojoji kan ceto mutane 360 da aka yi garkuwa da su a Borno
Zulum ya yabawa sojoji kan ceto mutane 360 da aka yi garkuwa da su a Borno

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya bisa nasarar ceto mutane 360 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a tsaunukan Mandara.

Rahotanni sun nuna cewa an ceto mutanen ne—maza, mata da yara—a wani farmaki na hadin gwiwa da sojojin Operation Hadin Kai suka gudanar a kudancin jihar Borno.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Gwamna Zulum ya bayyana aikin a matsayin “babbar bajinta da nuna jarumtaka da kwarewa,” yana mai cewa hakan na nuna ci gaban amfani da bayanan sirri wajen yaki da ta’addanci a Arewa maso Gabas.

Zulum ya kuma gode wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da shugabannin soji, da dakarun da suka shiga aikin ceto, yana mai cewa jajircewarsu ya sake kawo fata ga al’ummomin da abin ya shafa.

Ya kuma bukaci mazauna yankin da su ci gaba da zama cikin shiri tare da ba hukumomin tsaro hadin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen ci gaba da murkushe ‘yan ta’adda.

Gwamnan ya sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa sojoji ta hanyar kayan aiki da hadin gwiwa domin tabbatar da dawowar zaman lafiya mai ɗorewa a jihar Borno.

A halin yanzu, rahotanni sun ce ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro a yankin domin kawar da ragowar cibiyoyin ‘yan ta’adda.
Brighton Secure Rising Nigerian Star Zadok Yohanna in Long-Term Deal
Brighton Secure Rising Nigerian Star Zadok Yohanna in Long-Term Deal

Premier League club Brighton & Hove Albion have completed the signing of promising Nigerian forward Zadok Yohanna from AIK Stockholm on a five-year contract.

The 18-year-old winger has committed his future to the Seagulls until June 2031 after an impressive spell in Sweden, where he rapidly progressed from youth football to the senior team following his move from Kaduna-based Ikon Allah Academy in 2025.

Yohanna's performances attracted interest from several Premier League sides, including Chelsea, Manchester City, and Newcastle United, but Brighton ultimately secured the youngster's signature.

Speaking after completing the transfer, Yohanna expressed gratitude for reaching a major milestone in his career.

> "I am very happy to join this club because I know where I came from. I really wanted to make my family proud, and I have done that," he said.

Widely regarded as one of Nigeria's most exciting emerging talents, Yohanna has also been linked with a future call-up by Eric Chelle to the Nigerian national team.

The move marks another significant step in the teenager's rapid rise from grassroots football in Nigeria to one of the world's most competitive leagues. Brighton are expected to continue nurturing his development as he aims to establish himself in the Premier League and earn international recognition with the Super Eagles.
Russian Teen Mirra Andreeva Crowned Roland Garros Champion
Russian Teen Mirra Andreeva Crowned Roland Garros Champion

Russian teenager Mirra Andreeva secured the first Grand Slam title of her career on Saturday after defeating Polish qualifier Maja Chwalinska 6-3, 6-2 in the women's singles final at the French Open.

At just 19 years old, Andreeva became the youngest women's champion at Roland Garros since Monica Seles won her third consecutive title in Paris at age 18 in 1992. The victory also made Andreeva the first player born after 2005 to win a Grand Slam singles title.

The Russian star added the prestigious Coupe Suzanne Lenglen trophy to her growing collection, having already claimed two WTA 1000 titles earlier in her young career.

Despite the defeat, Chwalinska enjoyed a remarkable tournament run. Starting from the qualifying rounds, the world No. 114 won nine matches to become the first qualifier in the Open Era to reach a French Open women's singles final. Her impressive performance is expected to propel her to No. 21 in the world rankings, securing her place in future major tournaments.

The final began nervously, with both players struggling to settle under windy conditions on Court Philippe-Chatrier. Andreeva earned an early break, only for Chwalinska to respond immediately. The pair exchanged breaks several times before the Polish player briefly took a 3-2 lead.

However, Andreeva gradually gained control of the match, using powerful groundstrokes and consistent serving to claim the opening set 6-3. She maintained her momentum in the second set, racing into a commanding lead as Chwalinska battled to keep pace.

Although the Polish qualifier showed determination by breaking back when Andreeva served for the match, the Russian teenager quickly regained control. Andreeva sealed victory in the following game with a brilliant backhand winner before collapsing to the clay in celebration.

The triumph marks the biggest achievement of Andreeva's career so far and establishes her as one of the brightest young talents in world tennis.