Ministan Tsaron Cikin Gida na Isra’ila, Itamar Ben-Gvir, ya yi kira da a kashe Falasɗinawa tsakanin 30 zuwa 40 a Gaza a kowane dare, ciki har da mutanen da ba sa haifar da barazana kai tsaye a lokacin.
Ben-Gvir ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da tsohon fursunan Isra’ila, Rom Braslavski. Ya kuma yi kalaman da suka janyo suka, inda ya ce wasu Falasɗinawa “ba su cancanci rayuwa ba”.
Ministan ya soki matakin Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na rage hare-haren soji a Gaza karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai neman a dawo da kisan gilla da aka kai wa wasu mutane da ake zargi.
Ben-Gvir ba shi da ikon bayar da umarnin kai tsaye ga rundunar sojin Isra’ila, amma yana cikin majalisar tsaron Isra’ila da ke taka rawa wajen tsara manufofin tsaro da yaki.
Ya kuma bayyana goyon bayansa ga Falasɗinawa su bar Gaza na dindindin tare da kafa sabbin matsugunan Isra’ila a yankin.
Kalaman nasa sun sake jawo suka daga masu rajin kare hakkin bil’adama da masana shari’ar kasa da kasa, wadanda suka yi gargadin cewa tilasta wa Falasɗinawa barin Gaza na iya zama laifi na korar al’umma daga gidajensu.

0 $type={blogger}:
Post a Comment