An gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasdinawan a biranen Turai

An gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasdinawan a biranen Turai

Dubun dubatar mutane ne suka gudanar da zanga-zanga a Kasashen Turai, suna neman a yi adalci kan Kisan da Israi'la ke cigaba da yi a Gaza duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma.

Dubun dubatar mutane ne suka gudanar da jerin gwano a biranen nahiyar Turai, inda suke yin Allah wadai da yakin kisan kare dangi da Isra'ila ke yi a Gaza tare da neman daukar tsauraran matakai a duniya kan ci gaba da keta haddin da Amurka ta yi na tsagaita bude wuta.

Zanga-zangar da aka gudanar domin tunawa da ranar hadin kai da al'ummar Palasdinu ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Asabar, ta zo ne a daidai lokacin da adadin wadanda suka mutu a yakin da Isra'ila ta yi a Gaza ya zarce mutane 70,000.

Wadanda harin ya rutsa da su na baya-bayan nan sun hada da yara maza biyu masu shekaru takwas da 10, wadanda aka kashe a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a garin Bani Suheila da ke gabashin Khan Younis a kudancin Gaza.

A babban birnin kasar Faransa, Paris, kimanin mutane 50,000 ne suka yi tattaki a kan manyan titunan birnin, suna rera taken "Gaza, Gaza, Paris na tare da ku" da "Daga Paris zuwa Gaza, mun jajurce!"

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: