Yan bindiga sun kai hari a wani cocin dake jihar Kogi, inda suka yi garkuwa da Fasto da wasu masu ibada

Yan bindiga sun kai hari a wani cocin dake jihar Kogi

'Yan bindiga sun kai hari a wani cocin dake jihar Kogi, inda suka yi garkuwa da Fasto da wasu masu ibada.

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da harin da aka kai da sanyin safiyar yau lahadi a wani cocin Cherubim da Seraphim da ke Ejiba a karamar hukumar Yagba ta yamma a jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kingsley Fanwo ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi a Lokoja, inda ya yi kakkausar suka ga lamarin.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, ‘yan bindigar da suka kaddamar da harin, sun yi garkuwa da faston da matarsa ​​da wasu masu ibada.

Harin ya jefa al’ummar Ejiba cikin firgici, inda rahotanni suka ce mazauna garin sun tsere domin neman tsira.

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: