'Yar wasan Kungiyar kwallon kafar Mata ta Najeriya, Chiamaka Nnadozie ta zo ta hudu a kyautar Balllon d'or na 2025

'Yar wasan Kungiyar kwallon kafar Mata ta Najeriya, Chiamaka Nnadozie ta zo ta hudu a kyautar Balllon d'or na 2025

Mai tsaron ragan tawagar Mata ta Kungiyar kwallon kafar Najeriya, Super Falcons Chiamaka Nnadozie tazo ta hudu a kyautar Balllon d'or da ake zabar mata masu tsaron raga 5 da suka nuna bajinta a kowane shekara.

Mai tsaron ragar Kungiyar kwallon kafar Ingila da Chelsea, Hannah Hampton ce tazo ta daya yayin da Ann-Katrin Berger Mai tsaron ragar tawagar Jamus ta zo ta 2 sai Cata Coll ta kasar Sipaniya a matsayi na uku yayin da Chiamaka Nnadozie ke mataki na hudu sai Daphne van Domselaar Mai tsaron ragar Netherlands a matsayi na 5.

An gudanar da bikin bayar da kyautar ne a daren jiya litini a birnin Paris na kasar Faransa kamar yadda aka saba gudanar, inda Dan wasan PSG da faransa Ousmane Dembele ya lashe kyautar Balllon d'or a bangaren maza yayin da 'yar wasan Kungiyar kwallon kafar Mata ta Barcelona da Sifaniya, Aitana Bonmati ta lashe kyautar a bangaren Mata karo na uku.


SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: