Rukunin Biyu na ‘Yan Najeriya da Aka Kwashe daga Afirka ta Kudu Sun Isa birnin Legas.

Rukunin Biyu na ‘Yan Najeriya da Aka Kwashe daga Afirka ta Kudu Sun Isa birnin Legas.

Gwamnatin Tarayya ta kwashe wasu ‘yan Najeriya 66 daga Afirka ta Kudu, a wani mataki na ci gaba da taimaka wa ‘yan ƙasar da hare-haren kyamar baki suka shafa a ƙasar.

Mutanen da aka dawo da su, waɗanda su ne rukuni na biyu na waɗanda aka kwashe, sun isa filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas a daren Laraba da misalin ƙarfe 8:50 na dare.

An amince da wannan shirin kwashe ‘yan ƙasar ne daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bayan sake barkewar hare-haren da ake kai wa baƙi a Afirka ta Kudu.

Wannan shi ne karo na biyu na aikin, bayan an dawo da ‘yan Najeriya 258 a ranar 11 ga watan Yuni ta jirgin haya na kamfanin Air Peace.

Ma’aikatar Harkokin Waje ta tabbatar da cewa an dawo da mutane 66 a wannan mataki na biyu.

Hukumar ‘Yan Najeriya mazauna ƙasashen waje (NiDCOM) ta bayyana cewa shugaban kamfanin ValueJet, Kunle Soname, ne ya taimaka wajen shirya jirgin, yayin da jami’an Ofishin Jakadancin Najeriya a Afirka ta Kudu suka raka waɗanda aka kwashe.

NiDCOM ta yaba wa Shugaba Tinubu bisa amincewa da aikin kwashe mutanen, tare da tabbatar da cewa duk wani ɗan Najeriya da ya yi rajista kuma yake son komawa gida daga Afirka ta Kudu za a taimaka masa ya dawo.

Hukumar ta kuma sanar da tallafin da aka tanadar wa waɗanda suka dawo. ‘Yan asalin Jihar Imo da ke cikin waɗanda aka kwashe za su samu naira miliyan ɗaya kowanne daga Gwamnan jihar, Hope Uzodimma.

Kamfanin MTN Nigeria ya bayar da katin SIM kyauta da kuma data na naira 50,000 ga kowane mutum, sannan an saka naira 100,000 a asusun bankin kowane wanda aka dawo da shi.

Fasto Bolaji Idowu na cocin Harvesters International Christian Centre shi ma ya ba kowanne daga cikin waɗanda aka kwashe naira 100,000.

Waɗanda suka dawo sun nuna godiya ga gwamnatin Najeriya da sauran waɗanda suka taimaka wajen ganin sun dawo gida lafiya.

Jami’an NEMA, Hukumar ‘Yan Gudun Hijira da Masu Kaura, Hukumar Shige da Fice ta Najeriya, FAAN da jami’an tsaro sun kasance a filin jirgin domin tarɓar waɗanda suka dawo da kuma yin rajistar su.

0 $type={blogger}: