Haaland ya ci kwallaye biyu yayin da Norway ta doke ƙasar iraq a gasar cin kofin duniya na 2026.

Haaland ya ci kwallaye biyu yayin da Norway ta doke ƙasar iraq a gasar cin kofin duniya na 2026.

Dan wasan gaba Erling Haaland ya ci kwallaye biyu yayin da Norway ta fara gasar Kofin Duniya ta 2026 da nasara bayan ta doke Iraq da ci 4-1 ranar Talata.

Dan wasan na Manchester City ne ya fara jefa kwallo a ragar Iraq a minti na 29 a birnin Boston, amma Iraq ta dawo da martani ta hannun Aymen Hussein wanda ya rama da kai.

Haaland ya sake bai wa Norway damar nasara kafin a tafi hutun rabin lokaci bayan ya ci gajiyar kuskuren da ‘yan wasan bayan Iraq suka yi, lamarin da ya kai yawan kwallayen da ya ci wa kasarsa zuwa 57 a wasanni 51.

Daga baya Norway ta kara tazarar kwallaye bayan Leo Østigård ya ci ta uku da kai, kafin a samu kwallo ta hudu bayan wani kuskuren dan wasan Iraq da ya zura kwallon a ragar ƙasarsa.

Nasarar ta sanya Norway zama ta daya a rukunin I bisa bambancin kwallaye, inda take da maki uku daidai da Faransa wadda ta doke Senegal da ci 3-1.

Norway za ta kara da Faransa a wasanta na gaba a ranar 22 ga Yuni a birnin New Jersey.

Iraq, wadda ta samu gurbin gasar a matsayin kungiya ta karshe, tana buga gasar Kofin Duniya ne karo na farko tun bayan shekarar 1986.

0 $type={blogger}: