Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya gargadi Amurka cewa duk wani hari da za a kai wa kasarsa zai haifar da " mumunar yaki da zai shafi yankin gabas ta tsakiya".
Ya fadi haka ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ke cigaba da tara jiragen yaƙin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya da nufin kaddamar da harin akan Jumhuriyar musulci ta Iran.
"Ya kamata su sani cewa idan suka fara yaki a wannan karon, to zai zama yaki ne da zai shafi yankin baki daya," in ji shugaban kolin mai shekaru 86, a Lokacin wani taro da aka yi a birnin Tehran a yau Lahadi.
Shugaban kolin na Iran ya Kuma zargi Amurka da nufin kwace albarkatun man fetur da iskar gas na kasarsa.
_6.jpeg)
0 Comments:
Post a Comment