Rahotanni daga kafar yada labarai na PressTV sun bayyana cewa Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta kai hare-hare kan wasu wuraren masana’antu da ake dangantawa da Amurka da Isra’ila, a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren da aka kai kan muhimman ababen more rayuwa na Iran.
Rahoton ya ce matakin ya biyo bayan gargadin da jami’an Iran suka yi na cewa za su mayar da martani kan duk wani hari da aka kai kan cibiyoyinsu, musamman ma wuraren makamashi da na nukiliya.

0 Comments:
Post a Comment