Kwamishinan kimiya da fasaha na jihar Kano ya yi murabus Saboda ikirarin da ya yi cewa gwamnatin jihar ta kauce ma akidar da aka zabe ta a kai

Kwamishinan kimiya da fasaha na jihar Kano ya yi murabus

Kwamishinan kimiya da fasaha na jihar Kano ya yi murabus Saboda ikirarin da ya yi cewa gwamnatin jihar ta kauce ma akidar da aka zabe ta a kai.

Kwamishinan kimiya da fasaha da kirkire-kirkire na jihar Kano, Hon. Yusuf Kofarmata, ya yi murabus daga mukaminsa na mamba a majalisar zartarwa ta jihar, saboda abin da ya bayyana a matsayin kaucewa akidar siyasar da ta kai gwamnati mai ci a matsayin da ta ke.

Kofarmata ya sanar da murabus din nasa ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, inda ya ce an dauki matakin ne bisa gaskiya da kuma sahihin ja-goranci.

“Na ajiye mukamina na kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta Jihar Kano, ba zan iya ci gaba da aiki a karkashin gwamnatin da ta kaucewa akidar da ta kawo ta mulki ba,” inji shi.

Tsohon kwamishinan, wanda ya yi aiki a ma’aikatar ilimi mai zurfi da kuma ma’aikatar kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire, ya gode wa shugabannin jam’iyyar NNPP da kuma manyan jiga-jigan siyasa kan damar da ya samu wajen hidimta ma Jihar.


SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: