IPOB ta ja kunnen gwamnoni, tare da shelanta dokar zama a gida dole a Jihohin inyamurai dake Kudu maso Gabashin Najeriya

IPOB ta ja kunnen gwamnoni, tare da shelanta dokar zama a gida dole a Jihohin inyamurai dake Kudu maso Gabashin Najeriya

IPOB ta ja kunnen gwamnoni, tare da shelanta dokar zama a gida dole a Jihohin inyamurai dake Kudu maso Gabashin Najeriya.

Masu fafutukar kafa kasar Biafra sun jajirce kan gwamnonin yankin Kudu maso Gabas, inda suka ayyana dokar ta-baci a duk fadin yankin a ranar Litinin domin nuna rashin amincewarsu da rufe babbar kasuwar Onitsha da gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo ya yi.

Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra ta yi kira ga ‘yan kasuwa da masu safara da bankuna da makarantu da ma’aikatun gwamnati da kowane bangare a fadin jihohin Anambra da Abia da Imo da Enugu da Ebonyi da sauran su, da su kiyaye wannan dokar ta hadin gwiwa cikin lumana.

A halin da ake ciki, Soludo ya ba da umarnin sake fasalin kasuwar nan take bayan rufewar mako guda.

Umarnin ya biyo bayan ziyarar da gwamnan ya kai kasuwar ne a karshen mako, inda ya koka da cewa “kasuwar da ta fi kowacce girma a Afirka ta Yamma ta samu rauni Saboda rashin zamanantar da ita, Inda ya kara da cewa kasuwar ta mutu a sanadin haka.

Da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki da ’yan kasuwa a gidan "Light House" da ke Awka a ranar Juma’a, Soludo ya ce “Babban Kasuwar Onitsha a halin da take ciki yanzu ba ta aiki, mun yi wannan binciken, babbar kasuwar ba ita ce yadda aka tsara ta ba, a zahiri ta mutu.

"Na tuna wani lokaci a ƙarshen Shekarun 70s lokacin da kasuwa ta kasance abin koyi na inganci, tare da manyan tituna da ke ba da damar manyan motoci da masu siyayya su motsa cikin 'yanci. 
A yau, wannan tsari ya maye gurbin da hargitsi. Idan mutane ba za su iya yin kiliya ba, ba za su iya yin siyayya ba. 
A ƙarshen 70s, manyan motoci sun kasance suna shiga kasuwa; an samar da manyan wuraren ajiye motoci. Yau, wannan ya tafi."

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: