Babu sassauci ga masu taimakawa wa abokan gabanmu, inji babban Alkalin kasar Iran.

Babu sassauci ga masu taimakawa wa abokan gabanmu, inji babban Alkalin kasar Iran.

Babban alkalin kasar Iran ya gargadi masu zanga-zangar wadandada suka fito kan tituna a lokacin da ake fama da rikicin tattalin arziki, cewa ba za a yi sassauci ga wadanda ke taimakawa abokan gaba akan cutar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba, yana mai zargin Amurka da Isra'ila da Kara ingiza hargitsi a kasar.

"Bayan sanarwar da Isra'ila da shugaban Amurka suka yi, babu wani uzuri ga masu zuwa kan tituna domin tarzoma da tashe-tashen hankula," in ji babban mai shari'a Gholamhossein Mohseni Ejei da yake jawabi a ranar Laraba a wani sharhi kan zanga-zangar da kamfanin dillancin labarai na Fars ya gabatar.

A yayin da ake ci gaba da tashe tashen hankula, Iran na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar a makon da ya gabata cewa idan Tehran ta kashe masu zanga-zangar lumana da karfi, wanda al'adarsu ce, Amurka za ta kawo musu dauki.

Barazanar nasa - tare da jadadda cewa Amurka tana "kulle kuma a shirye take ta tafi" - ta zo ne watanni bakwai bayan da sojojin Isra'ila da na Amurka suka kai hare-hare kan wuraren nukiliyar Iran a yakin kwanaki 12.

Bugu da kari, Firayim Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya goyi bayan masu zanga-zangar a ranar Lahadin da ta gabata, yana mai gaya wa ministocin, "Abu ne mai yiyuwa mu kasance a daidai lokacin da al'ummar Iran ke daukar makomarsu a hannunsu."



SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: