Shugaban Majalisar Wakilai, Dr Tajudeen Abbas, ya yi Allah-wadai da tashin bam a jihar Zamfara da ya yi sanadin mutuwar mutane bakwai



Shugaban Majalisar Wakilai, Dr Tajudeen Abbas, ya yi Allah-wadai da tashin bam a jihar Zamfara da ya yi sanadin mutuwar mutane bakwai.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar din da ta gabata lokacin da wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka dasa bam a kan babbar hanyar Magami zuwa Dansadau a karamar hukumar Maru. 
Bom din ya fashe ne yayin da wata motar bas da ke dauke da fasinjoji ta bi ta kai, inda nan take ya kashe mutane bakwai.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata ta hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Musa Krishi, shugaban majalisar ya bayyana harin a matsayin na matsorata da rashin tausayi.

A cewarsa, “Abin takaici ne yadda aka kai harin jim kadan bayan da gwamnatocin Najeriya da na Amurka suka kaddamar da farmakin hadin gwiwa na yaki da ta’addanci a kasar, tare da kai hare-hare a maboyar ‘yan ta’adda a sassan Arewa maso Yamma a ranar Alhamis.”

Abbas ya ce Gwamnatin Tarayya ta bullo da sabbin tsare-tsare na tsaro don duba ayyukan ta’addanci, yana mai jaddada cewa za a ci gaba da dakile ayyukan ta’addanci, ‘yan fashi da sauran laifukan da ake yi wa jihar.

Ya kara da cewa ‘yan Najeriya sun kuduri aniyar marawa gwamnatin shugaba Bola Tinubu baya a yunkurinta na magance barazanar rayuwa da dukiyoyi a fadin kasar nan.

Abbas ya ce Gwamnatin Tarayya ta bullo da sabbin tsare-tsare na tsaro don duba ayyukan ta’addanci, yana mai jaddada cewa za a ci gaba da dakile ayyukan ta’addanci da na ‘yan fashi da sauran laifukan da ake yi a jihar.

Ya kara da cewa ‘yan Najeriya sun kuduri aniyar marawa gwamnatin shugaba Bola Tinubu baya a yunkurinta na magance barazanar rayuwa da dukiyoyi a fadin kasar nan.

Shugaban majalisar ya kuma yi alkawarin shirin majalisar na samar da tallafin da ya dace na majalisa da kasafin kudi domin tunkarar kalubalen tsaron kasar.

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: