Jerin Sabbin Shuwagabannin tsaron Najeriya da Tinubu ya nada da wadanda aka sauke.

Jerin Sabbin Shuwagabannin tsaron Sojin Najeriya da Tinubu ya nada da wadanda aka sauke.

A yau Juma'a ne Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da wata gagarumar garanbawul a shugabancin rundunar sojin kasar a wani bangare na kokarin karfafa rundunar tsaron kasar Najeriya.

A sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa Sunday Dare ya fitar ranar Juma’a, yace an nada Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon babban hafsan tsaron kasar, inda ya maye gurbin Janar Christopher Musa.

Ga jerin sabbin Shugabannin da waɗanda suka maye gurbinsu:

1. Babban Hafsan Tsaro: Laftanar Janar Olufemi Oluyede, wanda ya karbi ragamar mulki daga hannun Janar Christopher Musa.

2. Babban Hafsan Soji: Manjo-Janar W. Shaibu, ya maye gurbin Laftanar Janar Olufemi Oluyede.

3. Babban Hafsan Sojan Sama: Air Vice Marshal S.K. Aneke, wanda ya gaji AVM H.B. Abubakar.

4. Babban Hafsan Sojin Ruwa: Rear Admiral I. Abbas, ya karbi ragamar mulki daga Rear Admiral E. A. Ogalla.

5. Shugaban hukumar leken asiri na tsaro: Manjo-Janar E.A.P. Undiendeye, wanda ke rike da mukaminsa.

Wannan sauyi dai na daga cikin kokarin da shugaba Bola Tinubu yayi na karfafa tsarin tsaron kasa na Najeriya.


SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: