Amurka ta haramta wa tawagar Hukumar kwallon kafar kasar Iran shiga kasar

Amurka ta haramta wa tawagar Hukumar kwallon kafar kasar Iran shiga kasar

Amurka ta haramta wa tawagar Hukumar kwallon kafar kasar Iran shiga kasar domin halartan bikin kaddamar da jadawalin gasar cin kofin duniya da za ayi kasar a 2026, a cewar kakakin hukumar kwallon kafa ta Iran (FFI), Amir-Mehdi Alawi.

Daga cikin wadanda abin ya shafa har da shugaban FFI Mehdi Taj, da babban koci Amir Ghalenoei, da kuma wasu jami'an hukumar guda bakwai, in ji kakakin, kamar yadda jaridar Shargh ta ruwaito.

Yanzu dai hukumar ta FFI na fatan shawo kan shugaban hukumar ta FIFA Gianni Infantino ya janye matakin.

Kakakin ya yi tunanin Infantino zai dage haramcin nan da makonni biyu masu zuwa.

A ranar 5 ga watan Disamba ne za a yi jadawalin gasar cin kofin duniya na 2026 a birnin Washington.

Tun a baya an nuna damuwa game da dokar hana shige da fice da shugaban Amurka Donald Trump ya sanya wa Iraniyawa saboda takun saka da ke tsakanin Kasashe biyu.


Haramcin na iya kawo cikas ga halartar 'yan wasan kasar Iran da suka cancanci buga gasar cin kofin duniya na 2026 a Amurka, Kanada, da Mexico.

A cewar masana harkokin wasanni, mai yiwuwa kungiyar da masu horar da su kansu ba za su sami matsala a wannan haramci ba, amma wasu jami’an hukumar ta FFI, da masu aiko da rahotannin wasanni, da magoya bayan kungiyar za su iya fuskantar haramcin shiga kasar.

Haka zalika Hukumar na FFI na fatan a gudanar da wasannin Iran a Kasashen Kanada ko Mexico ne ba a Amurka ba.

Iran da Amurka dai sun dade ba su da wata dangantaka ta diflomasiya kusan sama da shekaru 45, tun bayan juyin-juya halin kasar ta Iran.

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: