Salatul fatihi salatin Annabi ne wanda mabiya darikar tijjaniya suke karantawa a lokutan gudanar da wazifa da sauran ibadu na farilla da nafila domin neman kai gaisuwa da yabo ga fiyayyen halatta Annabi Muhammad (S.A.W).
Fassarar Salatul fatihi
اَللَّهُمَّ صَلِّ عَلى سَيِّدِنَا مُحَمَّدٍ
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYIDNA MUHAMMAD:
"Ya ALLAH! Kayi Salati Ga Shugabanmu ANNABI
MUHAMMADU S.A.W"
اَلْفَاتِحِ لِمَا أُغْلِقَ
*AL-FATIHI LIMA UGLIQA:
"Wanda Ya Bude Abinda Yake Boye(Kafin ANNABI
S.A.W Ya Bayyana Komai Yana Cikin Taskar ALLAH Sai Da Ya Zo Ya Bude)"
وَ اَلْخَاتِمِ لِمَا سَبَقَ
*WAL-KHATIMI LIMA SABAQA:
"Wanda Ya Zama Cikamakin Dukkan Annabawa Da Suka Gaba Ce Shi"
نَاصِرِ الْحَقِّ بَالْحَقَّ
*NASIRIL HAQQI BIL HAQQI:
"Wato Shi ANNABI (S.A.W), Mai Taimakon Gaskiya
Da Gaskiya Ne,
Qur'ani Yana Cewa:'WA AMINU BIMA NUZILA ALA
MUHAMMADIN WAHUWAL HAQQU"
وَ الْهَادِي إلى صِرَاطِكَ الْمُسْتَقِيمِ
*WAL HADI ILA SIRADIKAL MUSTAQIM:
"Mai Shiryarwa Zuwa Hanya Madaidaiciya, Haka
ALLAH(S.W.T) Ya Fada Masa:'WA INNAKA LA
TAHDI ILA SIRADIL MUSTAQIM"
وَ عَلَى آلِهِ حَقَّ قَدْرِهِ و مِقْدَارِهِ الْعَظِيم
*WA ALA ALIHI HAQQA QADRIHI WAMIQDARIHIL'AZIM:
"Ya ALLAH Idan Zaka Masa Salatin Ka Sanya Hadda
Mutanen Gidansa, Kuma Ka Masa Salatin.
Gwargwadon Girmansa a Wajenka, Dama Kai kadai Kasan
Shi, Ka Kuma San Girmansan Nan Dai Wanda Ya Kai
Matuqa"
Wannan Ita Ce SALATUL FATIH Da Wasu Suke Zagi,
Dukkanta Tana Cikin Qur'ani Mai Girma, Kuma
Dukkan Lafuzan Cikinta Daukakar Darajar ANNABI
(S.A.W) ne, Ba Qasqantar Da shi bane, ballantana ku
Qita har ma wasu suna zagin ta,
Allah ya bamu Albarkan Salatil Fatihi Bijahi (S.A.W)
0 Comments:
Post a Comment