Amirul hajj na Jihar Jigawa kuma Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hameem Nuhu Sunusi, ya sanar da cewa alhazan jihar da suka halarci aikin Hajjin shekarar 2026 za su fara komawa Najeriya daga ranar 6 ga watan Yuni bayan kammala ibadar Hajji.
Sarkin ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai ma alhazan jihar ta Jigawa a masaukinsu dake Makkah, inda ya taya su murnar kammala ibadun Hajji cikin nasara.
Ya yabawa alhazan bisa nuna ladabi da hakuri da biyayya ga dokokin da suka jagoranci gudanar da aikin Hajjin, yana mai cewa halayensu sun nuna kyakkyawan wakilci ga jihar.
Sarkin ya kuma gargadi alhazan da su bi ka’idojin kamfanonin jiragen sama dangane da kaya yayin da ake shirye-shiryen komawarsu gida. Ya bukace su da kada su wuce iyakar kilo 23 na kayan da ake lodawa da kuma kilo 8 na kayan hannu domin kauce wa tsaiko ko asarar kaya a filin jirgin sama.
Yayin da yake taya su murnar cika daya daga cikin ginshikan Musulunci, Sarkin ya roke su da su ci gaba da yi wa Jihar Jigawa da Najeriya addu’o’in zaman lafiya da hadin kai da ci gaba da samun shugabanci nagari.
A halin yanzu, hukumomin da ke kula da aikin Hajji na ci gaba da kammala shirye-shiryen da za su tabbatar da dawowar alhazan cikin tsari da kwanciyar hankali.

0 $type={blogger}:
Post a Comment