Hare-haren Jiragen Sojin Saman Najeriya ya Kashe ‘Yan Ta’adda da Dama a Dajin Sambisa.

Hare-haren Jiragen Sojin Saman Najeriya ya Kashe ‘Yan Ta’adda da Dama a Dajin Sambisa.

Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF) ta kaddamar da hare-haren jiragen sama akan maboyar ‘yan ta’adda a Dajin Sambisa, inda aka kashe da dama daga cikinsu.

Rahotanni sun bayyana cewa harin ya faru ne ta bangaren sama na rundunar Operation Hadin Kai, inda aka kai hare-haren kan wuraren da ‘yan ta’addan ke fakewa a yankin Yuwe da ke cikin dajin. 
An bayyana hare-haren a matsayin na musamman kuma bisa sahihan bayanan leken asiri.

Hare-haren sun yi sanadin kashe ‘yan ta’adda da dama tare da tarwatsa ayyukansu a yankin. 
Duk da haka, ba a bayyana adadin wadanda aka kashe ba, amma an ce farmakin na daga cikin kokarin da sojoji ke yi na dakile ayyukan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas na kasar.

Dajin Sambisa ya dade yana zama mafakar kungiyoyin ta’addanci kamar Boko Haram da ISWAP, lamarin da ya sa rundunar soji ke yawan kai hare-hare domin rage karfinsu.

A kwanakin baya ma, irin wadannan hare-hare sun mayar da hankali wajen lalata maboyar ‘yan ta’adda, cibiyoyin ajiyar kayan yaki da kuma wuraren gudanar da ayyukansu, wanda ke taimakawa wajen rage karfin kungiyoyin a yankin.

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: