Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce irin hasarar rayukan Al'umma da Isra'ila ta yi a zirin Gaza ya sosa rayuwakan Al'ummar duniya da zuciyoyin Al'ummar musulmi.
Ya yi jawabin ne a wani taron tattaunawa da Kafar talabijin na Al Jazeera ya shirya a birnin Doha, babban birnin kasar Qatar a yau asabar, a a daidai lokacin da ake cigaba da samun takun saka tsakanin ƙasar Iran da Amurka.
Taron, wanda zai gudana daga ranar 7 zuwa 9 ga watan Fabrairu, zai yi dubi kan irin sauyin yanayin siyasar yankin gabas ta tsakiya, bisa la'akari da sakamakon yakin kisan Ƙare dangi da Isra'ila ta yi a zirin Gaza, da kuma muhimmiyar rawar da ta taka wajen sake fasalin yanayin siyasa a kasar Syria, tun daga faduwar gwamnatin Assad, da tattaunawa kan ma'aunin ikon yankin da na kasa da kasa, da kuma tasirinsu kan makomar yankin da dangantakar kasashen duniya.

0 Comments:
Post a Comment