Netanyahu ya amince da gayyatar Donald Trump domin shiga kwamitin zaman lafiya na Gaza

Netanyahu ya amince da gayyatar Donald Trump domin shiga kwamitin zaman lafiya na Gaza

Firayim Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya amince da gayyatar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi masa na shiga cikin "kwamitin zaman lafiya" na yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

Ofishin shugaban na Isra'ila ne ya sanar a shafinsa na sada zumunta a jiya Laraba, Inda yace, Netanyahu zai shiga wannan kwamiti, duk kuwa da cewa an kaddamar da shine a wani bangare na yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Kungiyar Hamas kashi na biyu na kawo karshen yakin kisan kare dangi da Isra'ila ke yi a Gaza.

Trump ya gayyaci shugabannin duniya da dama don shiga kwamitin, wanda ya yi hasashen zai sa ido wajen "sake gina zirin Gaza da mayar da hankalin wajen saka hannun jari a yankin.

Sai dai Koyaya, shigar Netanyahu zai ƙara damuwa game da haƙiƙanin wannan kwamitin, wanda Trump zai jagoranta?


SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: