Kotu ta ba tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello izinin tafiya zuwa Ƙasa mai tsarki domin yin aikin Ummarah.

Kotu ta ba tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello izinin tafiya zuwa Ƙasa mai tsarki domin yin aikin Ummarah.

Kotu ta ba tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello izinin tafiya zuwa Ƙasa mai tsarki domin yin aikin Ummarah.

A ranar Alhamis ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta amince da bukatar da tsohon gwamna Yahaya Bello na Kogi ya yi na tafiya birnin Makkah na kasar Saudiyya domin gudanar da aikin Ummarah a kwanaki 10 na karshen watan Ramadan a kasa mai tsarki.

Mai shari’a Emeka Nwite ya amince da bukatar ne bayan lauyan tsohon gwamnan, Joseph Daudu, SAN, ya gabatar da bukatar a kan haka.

Babban Lauyan ya bayyana cewa, bukatar ta nemi a ba da umarni da kuma ba da izinin sakin Fasfo na kasa da kasa na wucin gadi don ba shi damar zuwa Saudiyya don yin aikin Ummarah a watan Ramadan na bana, wanda zai fara a ranar 18 ga watan Fabrairu kuma ya kare a ranar 19 ga Maris.

Kemi Pinheiro, SAN, wacce ta bayyana a matsayin lauyar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, ba ta ki amincewa da bukatar ba.

Tun da farko a lokacin da kotu ta ba tsohon gwamnan damar bayyana kwanaki nawa yake da niyyar yi a kasar waje, ya ce duk da ya so ya yi kwanaki 30 a kasa mai tsarki, amma ya tuna da shari’ar da EFCC ke yi masa.

Bello ya ce, duk da cewa shekaru takwas da suka gabata bai yi tafiya a wajen Najeriya ba, amma zai yi kwanaki 10 na karshen watan Ramadan a Makka don yin addu’a ga Allah.

SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: