Shugaban Amurka Donald Trump ya isa kasar Masar domin taro game da kawo karshen yakin Gaza.

Shugaban Amurka Donald Trump ya isa kasar Masar domin taro game da kawo karshen yakin Gaza.

Shugaban Amurka Donald Trump ya isa kasar Masar domin taro game da kawo karshen yakin Gaza.

Bayan ya gabatar da Jawabi a majalisar dokokin Isra'ila, shugaban Amurka Donald Trump ya isa kasar Masar inda shugabannin kasashen duniya suka hallara domin taro akan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.
Ana sa ran Trump zai tattauna da shuwagabannin larabawa game da yadda za'a kawo karshen yakin gaba daya da kuma sake gina zirin na Gaza.

Haka zalika a yau litinin Israi'la ta fara sakin Falasdinawa da ake tsare da su a gidajen yari na Isra'ila bayan da kungiyar Hamas ta sako daukacin fursunonin Isra'ila 20 da ke tsare a zirin Gaza a wani bangare na yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Tun bayar sanar da amincewar bangarorin biyu game da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza Falasdinawa ke ci gaba da komawa sauran gidajensu a arewacin Gaza yayin da ake bukatar agajin jin kai a cikin yankin da hare-haren bama-bamai Israi'la ya daidaita.

Yakin Isra'ila a Gaza ya kashe akalla mutane 67,869 tare da raunata 170,105 tun daga watan Oktoba na shekarar 2023. A kalla mutane 1,139 aka kashe a Isra'ila yayin harin da Hamas takai a ranar 7 ga Oktoba, 2023, kuma an kama kusan mutane 200.



SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: