Tarihin Marigayi Sheikh Jafar Mahmoud Adam

 


Tarihin Marigayi Sheikh Jafar Mahmoud Adam


An haifi marigayi Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam a garin Daura, a shekara ta 1962 (ko da yake wani lokacin yakan ce 1964). 

Marigayi Sheikh Ja'afar ya fara karatunsa na allo a gidansu, a wurin mijin yayarsa, Malam Haruna, wanda kuma dan uwansu ne na jini.

Daga nan kuma sai aka mayar da shi wajen wani Malam Umaru a wani gari wai shi Koza, kimanin kilomita 9 a arewa da Daura, wanda shi ma akwai dangantaka ta jini a tsakanin su, wanda kuma shi ne musabbabin zuwansa Kano.

Bayan sun zo Kano ne tare da wannan malami nasa, a shekara ta 1971 (ko 1972), sai suka zauna a makarantar Malam Abdullahi, wanda asalinsa mutumin jamhuriyar Nijar ne, amma yake zaune a unguwar Fagge a Kano.

Tun kafin zuwansu Kano, tuni marigayi Sheikh Ja'afar ya riga ya fara haddar Alkur'ani mai girma, wanda ya kammala a shekara ta 1978.

Bayan da Malam ya kammala haddar Alkur'ani mai girma, kasancewarsa mai sha'awar ilimi, sai ya shiga makarantu biyu a lokaci daya a shekara ta 1980.

Ya shiga makarantar koyon Larabci ta mutanen kasar Misra a cibiyar yada al'adun kasar Misra, (Egyptian Cultural Centre), sannan kuma ya shiga makarantar manya da ba su yi boko ba ta Masallaci Adult Evening Classes, tunda a lokacin shekarunsa sun wuce shekaru na primary, amma duk da haka a wannan lokaci shi ne mafi kankanta a ajinsu.

Haka ya rika yin wannan karatu guda biyu: Waccan makarantar ya je ta da daddare bayan sallar isha'i, waccan kuma ta koyo harshen larabcin da yamma.

Ya kammala wadannan makarantu a shekara ta 1983. Wannan kuma shi ya ba shi damar shiga makarantar GATC Gwale a shekara ta 1984, kuma ya kammala a shekara ta 1988.

A shekara ta 1989, malam ya sami gurbin karatu a jami'ar musulunci ta Madinah, a inda ya karanta ilimin tafsiri da Ulumul Kur'an, wanda kuma ya kammala a shekara ta 1993. 

Sannan kuma Sheikh Ja’afar ya sami damar kammala karatunsa na digiri na biyu (Masters) a Jami’ar Kasa-Da-Kasa Ta Afrika da take Khartoum, Sudan.Sannan kuma, kafin rasuwarsa, ya riga ya yi nisa wajen karatunsa na digiri na uku, wato digiri da digirgir (PhD), a Jami’ar Usman Dan Fodiyo da take Sokoto. 

Daga cikin malamansa na ilimi, akwai malaminsa na farko, mutumin kasar Masar, Sheikh Abdul-Aziz Ali al-Mustafa, da kuma Malam Nuhu a unguwar Dandago, wanda malam ya karanci ilimi fikihun malikiyya da wadansu littattafai na hadisi a gurinsa, da kuma Malam Muhammad Shehu, mutumin Lokoja, wanda Malam ya karanci nahawu da sarfu da balaga da adab a wajensa.

Akwai kuma Sheikh Abubakar Jibrin limamin masallacin Juma'a na BUK, akwai kuma Dr. Ahmad Muhammad Ibrahim shi ma na jami'ar Bayero ta Kano.

Daga cikin malamansa na jami'a kuma, akwai Sheikh Abdurrafi'u da Dr. Khalid Assabt. Daga cikin karatuttukan da malam ya karantar da su, sun hada da tafsirin Alkur'ani mai girma, Kitabuttauhiid, Umdatul Ahkaam, Arba'una Hadiith, Kashfusshubuhaat, Bulugul Maraam, Riyaadussalihiin, Siiratun Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz, Siffatus Salaatun Nabiiy.

Wasu daga cikin daliban malam sun hada da Malam Rabi'u Umar R/Lemo da Malam Sani Abdullahi Alhamidi Dorayi da Malam Abdullah Usman G/Kaya da Malam Usman Sani Haruna da Malam Ibrahim Abdullahi Sani da Malam Ali Yunus Muhammad da Dr. Salisu Shehu da Malam Shehu Hamisu Kura da Malam Anas Muhammad Madabo.

Kafin rasuwarsa, malam ya fara gagarumin aikin rubuce tafsirinsa a harshen Hausa a karkashin wannan cibiya (Sheikh Ja'afar Islamic Documentation Centre).

Marigayi Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam ya rasu ranar juma'a 26/Rabii'u Awwal/1428 (13/04/2007) sakamakon harin da wadansu 'yan ta'adda suka kai masa, a daidai lokacin da yake jagorantar sallar asuba a masallacin Juma'a na Dorayi.

Ya rasu ya bar mata biyu, da 'yaya shida, yayin da aka haifa masa ta bakwai kwanaki 58 daidai bayan aiwatar da wannan kisan gilla a kansa. 

Dubun-dubatar mutane ne daga ko'ina cikin kasar nan suka halarci jana'izarsa, kuma an binne shi ne a makabartar Dorayi.

Allah ya ji kan sa ya gafarta masa, ya saka masa da gidan aljanna. Ameen summa Ameen

Article Translation in English Language.

The late Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam was born in the town of Daura, in the year 1962 (although sometimes he says 1964). 

The late Sheikh Ja'afar began his studies (makarantar Allo) in their house, in the presence of his sister's husband, Malam Haruna, who is also their blood relative. 
After that, he was transferred to a Malam Umaru in a town called Koza, about 9 kilometers north of Daura, who is also a blood relation between them, which is the reason for his coming to Kano.

After they came to Kano with this teacher of his, in the year 1971 (or 1972), they stayed in the school of Malam Abdullahi, who is originally from the Republic of Niger, but lives in Fagge neighborhood in Kano. Even before their arrival in Kano, the late Sheikh Ja'afar had already started memorizing the Holy Qur'an, which he completed in 1978. 
After Malam completed memorizing the great Qur'an, being interested in education, he joined two schools at the same time in 1980. 
He entered the Arabic learning school for the people of Egypt at the Egyptian Cultural Center, and he also entered the mosque's adult evening classes, since at that time he was over the age of primary, but still at this time he is the youngest in his class. 
He used to do this two studies: He went to that school at night after Isha prayer, and that one he learned Arabic language in the evening.

He graduated from these schools in 1983. This allowed him to join GATC Gwale in 1984, and he graduated in 1988. 
In the year 1989, the teacher received a scholarship at the Islamic University of Madinah, where he studied interpretation and Ulumul Qur'an, which he completed in the year 1993. 
And Sheikh Ja'afar was able to complete his Master's degree at the African International University in Khartoum, Sudan. 
The third, that is a PhD, at the Usman Dan Fodiyo University in Sokoto. 
Among his teachers, there is his first teacher, an Egyptian man, Sheikh Abdul-Aziz Ali al-Mustafa, and Mr. Nuhu in Dandago, who studied jurisprudence and other books of hadith in his place, and Mr. Muhammad Shehu, a man from Lokoja, from whom Malam studied grammar, eloquence and literature.

There is also Sheikh Abubakar Jibrin, the imam of BUK's Friday mosque, and Dr. Ahmad Muhammad Ibrahim is also from Bayero University in Kano. 
Among his university teachers, there are Sheikh Abdurrafi'u and Dr. Khalid Assabt. 
Among the books taught by the teacher, they include the interpretation of the Holy Qur'an, Kitabuttauhiid, Umdatul Ahkaam, Arba'una Hadiith, Kashfusshubuhaat, Bulugul Maraam, Riyaadussalihiin, Siiratun Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz, Siffatus Salaatun Nabiiy. 
Some of the teacher's students include Mr. Rabi'u Umar R/Lemo, Mr. Sani Abdullahi Alhamidi Dorayi, Mr. Abdullah Usman G/Kaya, Mr. Usman Sani Haruna, Mr. Ibrahim Abdullahi Sani, Mr. Ali Yunus Muhammad and Dr. Salisu Shehu and Malam Shehu Hamisu Kura and Malam Anas Muhammad Madabo. 
Before his death, the teacher started the great work of writing his commentary in Hausa language under this center (Sheikh Ja'afar Islamic Documentation Center). 
The late Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam died on Friday 26/Rabi'u Awwal/1428 (13/04/2007) as a result of an attack by some terrorists, while he was leading the morning prayer in Dorayi Juma mosque.

He died leaving two wives and six children, while his seventh was born exactly 58 days after the execution of this brutal murder against him. 
Tens of thousands of people from all over the country attended his funeral, and he was buried at the Dorayi cemetery. 
May Allah mighty God forgave him and grant him a jannatul firdaur. Ameen.



SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: