Ƙasashen Afirka Tara (9) Sun yi Nasaran Kaiwa Zagayen 'Yan 32 na Gasar Cin Kofin Duniya na 2026.

Ƙasashen Afirka Tara (9) Sun yi Nasaran Kaiwa Zagayen 'Yan 32 na Gasar Cin Kofin Duniya na 2026.

Afirka ta kafa sabon tarihi a gasar cin kofin duniya ta 2026, inda daga cikin ƙasashe 10 da suka samu damar shiga gasar, tara daga cikinsu sun samu gurbin zuwa matakin zagayen ‘yan 32.

An tabbatar da wannan nasarar ne bayan da Congo ta doke Uzbekistan da ci 3-1, yayin da Algeria ta yi kunnen doki 3-3 da Austria, lamarin da ya ba ƙungiyoyin biyu damar tsallakewa.

Kafin wannan lokaci, mafi yawan ƙasashen Afirka da suka taɓa kaiwa matakin fitar da gwani a gasar cin kofin duniya a lokaci guda sun kasance biyu kacal.

Bayan kwanaki 17 na gasar, ƙasashen Afirka da suka samu gurbin shiga zagayen ‘yan 32 sun haɗa da Morocco da Afirka ta Kudu, Senegal da Ivory Coast da Ghana da Cape Verde da Masar da Congo da Algeria.

Morocco, wadda ta zama ƙasar Afirka ta farko da ta kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin duniya na 2022, ta ci gaba da nuna ƙarfi bayan ta yi kunnen doki 1-1 da Brazil.

Congo ma ta kafa babban tarihi bayan ta kai zagayen fitar da gwani a karo na biyu a tarihinta. Yoane Wissa ya ci ƙwallaye biyu, yayin da Fiston Mayele ya ƙara ɗaya a nasarar da suka samu kan Uzbekistan.

Mayele ya ce wannan nasara abin alfahari ce ga ƙasarsu, yana mai cewa jama'ar Congo sun yi matuƙar farin ciki da wannan abin da suka cimma.

Algeria kuma ta samu tikitin wucewa ne bayan wani wasa mai ɗaukar hankali da Austria. Riyad Mahrez ya zura ƙwallo a ƙarshen lokaci, kafin Austria ta rama a lokacin ƙarin lokaci, amma kunnen dokin ya wadatar da ƙungiyoyin biyu.

Wissa ya bayyana cewa wannan nasarar na nuna cewa ƙwallon ƙafa a Afirka na ƙara samun ci gaba, musamman saboda sabbin matasa masu hazaka.

Ya ce yanzu duk wata ƙungiyar Afirka na iya yin mafarkin yin babban nasara a gasar duniya.

Gasar cin kofin duniya na 2026 ta zama wata muhimmiyar gasa da ta nuna ƙarfin ƙwallon ƙafa na Afirka a idon duniya.

0 $type={blogger}: