Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Mai Martaba Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga Musulmai da su kasance masu bin koyarwar addinin Musulunci ta gaskiya ta hanyar zama masu wanzar da zaman lafiya da sulhu da haɗin kai a cikin al’umma.
Da yake jawabi a wajen kaddamarwa tare da mika sabon masallaci na zamani da aka gina domin tunawa da cikar shekaru 80 na Asiwaju Khamis Badmus a birnin Osogbo a karshen mako, Sarkin Musulmi ya jaddada cewa fahimtar addini yadda ya kamata tana haifar da mutane masu ladabi da tausayi da kishin zaman lafiya.
Ya samu wakilci daga Shugaban Musulmi na Kudu maso Yamma (MUSWEN), Alhaji Rasak Oladejo, inda ya ce addini ya kamata ya sauya zuciyar mutum daga ƙiyayya zuwa soyayya, daga rikici zuwa fahimtar juna.
“Fahimtar addini ta gaskiya tana haifar da Musulmi masu ladabi, masu tausayi da wayewa, waɗanda ke gina zaman lafiya ba rushe shi ba,” in ji shi, yana mai ƙarfafa cewa Musulmi su zama “masu gina sulhu da zaman lafiya.”
Ya kuma bayyana cewa manufar masallaci ba kawai yin sallah biyar ta yau da kullum ba ce, illa ya zama cibiyar tarbiyya da ilimi da ci gaban al’umma.
A nasa jawabin, Babban Limamin kungiyar Ansar-u-Deen, Sheikh Abdulrahman Ahmad, ya ce masallaci ya kamata ya kasance cibiyar warware matsalolin zamantakewa da tattalin arziki da siyasa a cikin al’umma.
Ya yi bayani kan masallacin Quba da ke Madina, inda ya ce a farkon Musulunci masallatai ba wurin ibada kaɗai ba ne, har ma suna zama makaranta da ɗakin karatu da ma’aji da cibiyar bayanai da kotu har ma da ƙaramin majalisa da asibiti.
Ya ce koma bayan da aka samu a yau ya samo asali ne daga mayar da hankali kan tara dukiya fiye da ainihin manufar masallaci, wanda hakan ya taimaka wajen fuskantar matsaloli a cikin al’ummar Musulmi ta duniya.
Taron ya samu halartar manyan shugabannin addini da sarakunan gargajiya da kuma manyan ‘yan siyasa, ciki har da Oluwo na Iwo, Aragbiji na Iragbiji, da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Prince Olagunsoye Oyinlola, da sauransu.

0 $type={blogger}:
Post a Comment