'Yan ta'adda sun kashe mutum hudu tare da kona shaguna a jihar Neja.

'Yan ta'adda sun kashe mutum hudu tare da kona shaguna a jihar Neja.

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar da kashe mutane hudu tare da kona shaguna da ‘yan ta’adda suka yi a jihar.

‘Yan ta’addan sun kai farmaki kauyen Damala da ke gundumar Woko a karamar hukumar Borgu a ranar Asabar din da ta gabata, a wani harin da suka kai da sanyin safiyar ranar, lamarin da ya haifar da firgici a yayin da mazauna garin suka ruga ta hanyoyi daban-daban domin neman tsira.

Wata majiya a yankin ta ce an kuma sace wasu mutanen da ba a bayyana adadinsu ba yayin harin.


SHARE THIS

Author:

I am a blogger by passion and a Website developer by profession, I am currently the CEO of Hausalive.com.ng, a website that brings you a daily needful and useful contents.

0 Comments: